Katsina - Tsagerun yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kuma kai hari karamar hukumar Jibiya dake jihar Katsina da daren Talata, 8 ga watan Febrairu, 2022.
TVCNews ta ruwaito cewa yan bindigan sun hallaka DPO na ofishin yan sandan Magamar Jibiya da kuma wani hafsan Soja.
Hakazalika an ruwaito cewa wani kwamanda Soji ya jikkata.
Wannan ya faru ne lokacin da jami'an tsaron suka kai dauki cikin dare bayan samun labarin cewa yan bindiga sun shiga magamar Jibia suna harbe-harbe.
Kara karanta wannan
Yan bindiga sun hallaka mutum 10, sun sace Hakimi a jihar Katsina
Karamar hukumar Jibia na daya daga cikin kananan hukumomin dake fuskantar barazanar yan bindiga a jihar Katsina.
Har yanzu, hukumar yan sanda basu saki jawabi kan kisan jami'ian tsaron ba.
Ku dakaci karin bayani..
Haka a ranar Alhamis, 3 ga watan Febrairu, 2022 yan bindiga masu garkuwa da mutane suka dira garin Yangayya dake karamar hukumar Jibia a jihar Katsina cikin dare.
Premium Times ta ruwaito cewa yan bindiga sun kashe Dagacin garin tare da mutum hudu.
Wani mazaunin Jibia, Halilu Kabir, ya bayyanawa manema labarai cewa yan bindigan sun kwashe sa'o'i uku suna cin karensu ba babbaka.
Yace sun shigo kan babura kuma suka fara harbi. Yayinda suke bi gida-gida suka kashe mutum hudu da suke kokarin guduwa.
Asali: Legit.ng
ncG1vNJzZmigkarAonrLnp6irF6jtHC6xLCqaGlkaoJ0fJNmm5pllKq6qrrSmmSymZ5ir6q6w6KemmWjqrtut8Csn55llKW8brTAn6qapl2ovKutjJpkrJmSpLtutMCroKdlkWK3qq7ImmY%3D